Gwamnatin jihar Kebbi tana shirin zakulo hazikan matasa domin inganta basirar su

A ci gaba da tsare-tsare kan shirin da take yi domin ganin ta inganta rayuwar matasa ta hanyar zaburar da hikimarsu domin ganin sun dukufa akansa a yau Mataimakin Gwamnan jihar Kebbi Samaila Yombe Dabai ya jagoranci wani zama na tattaunawa domin tsara dabaru da suka inganta domin kai ga nassarar shirin .

Gwamnan jihar Kebbi Atiku Babudu ya bayar da umarni akan ganin cewa an zakulo tare da inganta tunanin hazikan matasa tare da al'umma da ke da basira na kere-kere ko kirkire-kirkire da zai amfani jama'ar jihar Kebbi da kasar Najeriya gaba daya.

A zaman da aka yi a ofishinsa da ke Cabinet Office Samaila Yombe ya mayar da hankali akan tsara dabaru wadanda za su kai ga nassara kamar yadda ake bukata.

Zaman tattaunawar ta yau ta hada da jagoran sassa na shirin da aka yi wa suna Skills Acquisation programme inda aka canja sunan zuwa Kebbi Youth Innovative Centre.

Tsarin shirin zai taimaka wa dubban matasa wajen zakulo tare da habbaka hazakarsu ta hanyar shigowar cikin tsarin ayyukansu daga sassa da aka tanada domin gudanar da shirin a karkashin kwamitin da aka tanada.

Ga masu shawara,aiko labari ko korafi ku rubuto zuwa isyakulabari@gmail.com Kaunace mu a Facebook https://www.facebook.com/isyakuweb Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN