Gwamnan jihar Kebbi Atiku Babudu ya bayar da umarni akan ganin cewa an zakulo tare da inganta tunanin hazikan matasa tare da al'umma da ke da basira na kere-kere ko kirkire-kirkire da zai amfani jama'ar jihar Kebbi da kasar Najeriya gaba daya.
A zaman da aka yi a ofishinsa da ke Cabinet Office Samaila Yombe ya mayar da hankali akan tsara dabaru wadanda za su kai ga nassara kamar yadda ake bukata.
Zaman tattaunawar ta yau ta hada da jagoran sassa na shirin da aka yi wa suna Skills Acquisation programme inda aka canja sunan zuwa Kebbi Youth Innovative Centre.
Tsarin shirin zai taimaka wa dubban matasa wajen zakulo tare da habbaka hazakarsu ta hanyar shigowar cikin tsarin ayyukansu daga sassa da aka tanada domin gudanar da shirin a karkashin kwamitin da aka tanada.
Ga masu shawara,aiko labari ko korafi ku rubuto zuwa isyakulabari@gmail.com Kaunace mu a Facebook https://www.facebook.com/isyakuweb Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com