'Yar shekara 7 ta shiga tseren gudu har kilomita 10

Wata Yarinya mai shekara 7 ta shiga gasar gudun tseren falfalaki na Lagos .Damilola Oluwaseun ta zura gudu ne har na kilomita 10 daga cikin kilomita 42.Yarinyar dai ta shiga gudun ne a kilomita 32 wanda yake a karshen gadan Lekki da ke a garin na Lagos ta ce tayi murnar kasancewa a cikin gasar.
An fara gudun ne daga babban filin wasar Lagos kuma aka kammala shi a Eko Atlantic City.

Kamfanin dillancin labarai ta Najeriya ta ruwaito cewa ,akalla 'yan kasashen waje 62 da 'yan tsere 102 a nan gida Najeriya suka shiga gasar da tun farko akayi rigistan mutane 55,000  daga kasashe 27 har da Najeriya.
Wanda yayi nassara na farko a gasar gudun ya tashi da kyautar Dalar Amurka 50,000 ,na biyu kuma ya sami kyautar dubu 40,000 na uku kuma ya sami dubu 30,000 na dalar Amurka.

Abraham Kiptom da Rhoda Jepokorir suka yi nassara a matakin kasa da kasa a rukunin Maza da Mata.Shi kuma Philip Sharubutu kare kambun sa ne yayi wanda ya ci a wannan gasar a bara a yayin da Emmanuel Gyang ya zo a lamba na biyu.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN