Hukumar ‘yan sanda ta jihar Lagas ta kama wani matashi mai
suna Sakiru Bello dan shekara 36 a bisa zargin kashewa da sassare jikin matar sa
Sharifat Bello uwar yara uku a ranar 13 ga watan Fabrairu 2017.
Jaridar Vanguard ta wallafa cewa Sikiru ya gaya wa ‘yan sanda
cewa bai yi niyyar kasha Sharifat ba kuma bas hi ne ya kasha ta ba ya ce abin
day a faru shine,ya kira matar tashi Sharifat a inda suka je bakin teku,a yayin
da suke dawowa ne a kan babur sai wani mai mota ya buge su,lamarin da ya sa suka
fadi kuma kan sharifat ya bugi kwalta.Ya ce bayan sun isa gida ne can da dare
sai ta fara koken cewa kan ta yana ciwo,yace ya kasa kai ta Asibiti ne domin
baya da kudi,kuma ba su shiri da Uwayen Sharifat, balle ya nemi taimako daga
wajen su,a cikin wannan yanayin ne matar tashi Sharifat ta mutu da dare.
A ci gaba da bayani ga ‘yan sanda,Sikiru ya ce bayan da ta
mutu da dare,sai ya rude ya rasa yadda zai yi,can sai tunani ya zo masa akan
cewa ya sassare ta ya sanya a cikin Ghana
must go sai ya je ya binne ta a wani gini da ba’a kammala ba inda ya binne
sassan jikin Sharifat a rami daban-daban.
Mahaifin Sharifat ya ce bayan basu gan sharifat ba har na
tsawon wani lokaci,sai suka tuntubi mijin nata Sikiru,amma basu gamsu da
martanin day a bayar ba,akan haka ne suka garzaya zuwa rukuni na “B” na
‘yan sandan jihar Lagos inda suka fara binciken da ya kai ga kamo Sikiru a cikin
garin Lagos bayan ya gaya wa surukan sa cewa yana Ibadan bayan sun tuntube shi
a wayan salula.
Har yanzu dai ‘yan sanda suna ci gaba da bincike akan wannan
mummunar rashin imani,da zarar an gama bincike ‘yan sanda za su gabatar das hi
a gaban Kuliya.