Shugaba Buhari Ya Tsawaita Hutun Da Ya Ke Yi a London

Shugaban Muhammadu Buhari ya kara wa’adin hutun da ya dauka wanda ya ke yi a birnin London da ke kasar Ingila.
Wannan ya na kunshe ne a wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban Femi Adesina ya wallafa a shafinsa na Facebook.
Adesina ya ce shugaban ya rubuta wa majalisa takardar neman tsawaita wa’adin hutu nasa domin ya samu damar yin gwaje gwaje da likitocin sa suka umarce shi ya yi.
Shugaba Buhari dai ya dauki hutun ne a ranar 19 ga watan Janairu, kuma a gobe Litinin, 6 ga watan Fabrilu ne ya kamata ya dawo gida Nijeriya. Toh sai dai sanarwar ba ta bayyana adadin ranakun da zai tsawaita hutun da su ba.
MUJALLARMU

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN