Kotu ta kwace Naira Biliyan 34 na Tsohuwar Ministan mai na Najeriya

Wata babbar Kotu a garin Lagos karkashin shugabancin Alkalin Kotun Mai shra'a (Justice) Muslim Hassan ta kwace kana ta halatta wa Gwamnatin tarayyar Najeriya Naira Biliyan 34 mallakin tsohuwar Ministan man fetur na Najeriya karkashin tsohuwar Gwamnatin Goodluck Jonathan Mrs Diezani Alison-Madueke.

Hukumar kama masu yi wa tattalin arzikin kasa ta'arnaki ta EFCC ce ta shigar da karar kuma ta bukaci Kotun ta kwace kudaden wanda bayan gabatar da shedu da cika matakai na shara'a,Kotu ta yanke hukuncin mika kudaden ga Gwamnatin tarayya.


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN