Wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton ‘yan Boko Haram ne sun kai wa
wasu matafiya a cikin mota farmaki akan hanyar su ta zuwa jahar Taraba
daga Maiduguri.
Motar na dauke ne da wasu daliban jami’ar Maiduguri da ke kan hanyarsu ta zuwa gida bayan da suka kammala jarrabawarsu tare da wasu mutanen daban.
Mayakan sun farwa motar, inda suka bude mata wuta suka kuma kashe mutane da dama yayin da yawa suka jikkata. Wasu kuma sun samu nasarar tserewa bayan da direban ya tsayar da motar.
Wani malamin jami’ar Maiduguri ya shaidawa Kafar yada Labarai na BBC cewa sun tabbatar da mutuwar dalibai biyu daga ciki, yayin da wasu uku kuma suna babban asibitin koyarwa na Maiduguri.
Baya ga daliban jami’ar, akwai kuma wasu mutane da suka mutu wadanda ba a san adadinsu ba zuwa yanzu.
Makonnin biyun da suka gabata ne kungiyar ta Boko Haram ta kai harin ta na farko a jami’ar ta Maiduguri inda mutane biyar suka rasa rayukan su,a ciki har da wani farfesa.
ALUMMATA
Motar na dauke ne da wasu daliban jami’ar Maiduguri da ke kan hanyarsu ta zuwa gida bayan da suka kammala jarrabawarsu tare da wasu mutanen daban.
Mayakan sun farwa motar, inda suka bude mata wuta suka kuma kashe mutane da dama yayin da yawa suka jikkata. Wasu kuma sun samu nasarar tserewa bayan da direban ya tsayar da motar.
Wani malamin jami’ar Maiduguri ya shaidawa Kafar yada Labarai na BBC cewa sun tabbatar da mutuwar dalibai biyu daga ciki, yayin da wasu uku kuma suna babban asibitin koyarwa na Maiduguri.
Baya ga daliban jami’ar, akwai kuma wasu mutane da suka mutu wadanda ba a san adadinsu ba zuwa yanzu.
Makonnin biyun da suka gabata ne kungiyar ta Boko Haram ta kai harin ta na farko a jami’ar ta Maiduguri inda mutane biyar suka rasa rayukan su,a ciki har da wani farfesa.
ALUMMATA
Tags:
LABARI