Jammeh ya wawushe dukiyar Gambia

Tsohon shugaban Gambia Yahya Jammeh ya batar da miliyoyin dalolin kasar kafin ya tsallaka ya fice, kamar yadda wani Jami’in sabon Shugaban Gambia Adama Barrow ya tabbatar.
Mai Ahmed Fatty mai ba Adama Barrow shawara ya ce Jammeh ya kwashe dukiyar Gambia da wasu motocin alfarma.
Jami’in ya ce a cikin makwanni biyu, tsohon shugaban kasar ya kwashe Dala miliyan 11 daga baitulmalin Gambia.
Fatty ya ce yanzu haka babu sisin kwabo a cikin asusun ajiyar kasar, yayin da aka nemi wasu motocin alfarmar gwamnati aka rasa.
A ranar Asabar ne Jammeh wanda ya shafe shekaru 22 yana mulki a Gambia ya fice zuwa kasar Equatorial Guinea inda ake tunanin zai ci gaba da rayuwa da iyalan shi.
Tuni dai sojojin kasashen Afirka ta Yamma suka mamaye sassan birnin Banjul domin tabbatar da zaman lafiya kafin isar sabon shugaban kasar Adama Barrow daga Senegal inda aka rantsar da shi.
Bayanai masu karo da juna na cewar, akwai wata yarjejeniya da aka tsara da za ta hana binciken tsohon shugaban amma ministan harkokin wajen Senegal ya ce ba shi da masaniya akai.
Wasu mutane sun fara sukar yarjejeniyar da ta bayyana cewar gwamnatin Gambia ba za ta dauki wasu matakan da za su ci zarafin tsohon shugaban ba ko kwace ma shi kadarori ba.

rfi hausa

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN