Bindigar wani jami’in DSS da ke aiki a fadar shugaba kasa ta yi harbi
bisa kuskure inda taji wa wata mata wadda itama ma’aikaciya ce ciwo a
cikinta, bayanta da cinyarta.
Lamarin ya faru ne a misalin karfe 2:30 na rana a jiya Laraba a dakin tarbar baki na fadar shugaban kasa, fannin ofishin gudanarwa.
Yayin da jami’in DSS din ke yunkurin cire harsashan da ke cikin bindigar kafin ya ajiye ta a wajen da ake binciken baki kafin su shiga harabar ofishin ne sai kawai bindigar ta yi harbi kuma anan take ta raunata matar wacce ita ma ke yunkurin shiga harabar ofishin.
Lamarin ya faru ne a misalin karfe 2:30 na rana a jiya Laraba a dakin tarbar baki na fadar shugaban kasa, fannin ofishin gudanarwa.
Yayin da jami’in DSS din ke yunkurin cire harsashan da ke cikin bindigar kafin ya ajiye ta a wajen da ake binciken baki kafin su shiga harabar ofishin ne sai kawai bindigar ta yi harbi kuma anan take ta raunata matar wacce ita ma ke yunkurin shiga harabar ofishin.
Tuni dai aka garzaya da matar zuwa asibitin da ke fadar shugaban kasa domin a yi mata magani.
(AL'UMMATA)
(AL'UMMATA)
Tags:
LABARI