HARBI DAGA BINDIGAR WANI JAMI'IN TSARO NA DSS YA RAUNATA MA'AIKACIYA A CIKIN FADAR SHUGABAN KASA

Bindigar wani jami’in DSS da ke aiki a fadar shugaba kasa ta yi harbi bisa kuskure inda taji wa wata mata wadda itama ma’aikaciya ce ciwo a cikinta, bayanta da cinyarta.
Lamarin ya faru ne a misalin karfe 2:30 na rana a jiya Laraba a dakin tarbar baki na fadar shugaban kasa, fannin ofishin gudanarwa.
Yayin da jami’in DSS din ke yunkurin cire harsashan da ke cikin bindigar kafin ya ajiye ta a wajen da ake binciken baki kafin su shiga harabar ofishin ne sai kawai bindigar ta yi harbi kuma anan take ta raunata matar wacce ita ma ke yunkurin shiga harabar ofishin.
Tuni dai aka garzaya da matar zuwa asibitin da ke fadar shugaban kasa domin a yi mata magani.
(AL'UMMATA)

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN