Gwamnatin tarayya ta daukaka karar da ke kalubalantar hukuncin da Mai
shari’a Kolawale Gabriel ya yanke da ke bukatar a saki shugaban
kungiyar shi’a Sheik Ibrahim El-Zakzaky da matarsa, tare da gina masa
gida a kowace jaha da ya so a fadin kasar nan. Hukuncin ya kuma bukaci a
biya matarsa diyyar naira miliyan 50.
Hukumar tsaron farin kaya, Ma’aikatar tsaro da ma’aikatar shari’a su suka kalubalanci hukuncin a kotun daukaka kara, da cewar alkalin ya yanke hukuncin ne bisa kuskure saboda ya hada kararraki daban daban a guri guda.
Daukaka karar ta kunshi laifuka 7 na shugaban kungiyar wanda ke tsare tun Disambar shekarar 2015.
A ‘yan kwanakin nan, mambobin kungiyar shi’an sun kara kaimi wajen yin zanga zanga, inda suke kira da a saki jagoran na su.
A zanga-zangar su ta karshe, ‘yan Shi’an sun gamu da fushin ‘yan sanda da su ka yi ta jefa musu barkonon tsohuwa.
ALUMMATA
Hukumar tsaron farin kaya, Ma’aikatar tsaro da ma’aikatar shari’a su suka kalubalanci hukuncin a kotun daukaka kara, da cewar alkalin ya yanke hukuncin ne bisa kuskure saboda ya hada kararraki daban daban a guri guda.
Daukaka karar ta kunshi laifuka 7 na shugaban kungiyar wanda ke tsare tun Disambar shekarar 2015.
A ‘yan kwanakin nan, mambobin kungiyar shi’an sun kara kaimi wajen yin zanga zanga, inda suke kira da a saki jagoran na su.
A zanga-zangar su ta karshe, ‘yan Shi’an sun gamu da fushin ‘yan sanda da su ka yi ta jefa musu barkonon tsohuwa.
ALUMMATA
Tags:
LABARI