An kama ‘yan fashi fiye da 400 a Kaduna

Yansandan a jihar Kaduna da ke a Arewacin Najeriya sun sanar da cafke ‘yan fashi sama da 400 wadanda ake zargi da laifin yin garkuwa da mutane da kuma satar shanu a cikin shekarar 2016.
Kwamishina ‘yansandan jihar, Mista Agyelo Abeh ne ya tabbatar da kama mutanen ya kuma shaida cewa sun kwato muggan makamai sama da 100 daga hannu ‘yan fashin.
Mista Agyelo ya ce tuni aka mika 384 daga cikin wadanda aka kama gaban kuliya, yayin da ake ci gaba da binciken sauran.
Matsalar satar shanu da kuma yin garkuwa da mutane ya zama ruwan dare gama gari a Najeriya a shekarun baya bayan nan.
RFI Hausa

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN