NAIJ.COM-Boko haram za ta kashe yan kungiyar ta da suka gudu a fagen daga
Shugabannin Boko Haram sunyi arazanar kashe duk mambansu da ya gudu daga dajin Sambisa a yankin arewa maso gabas.
Wannan barazanar na zuwa ne bayan rundunar soji Najeriya na wura way an Boko Haram din wuta a dajin.
Wani
dan banga a Damboa, mai suna Malam Abubakar Buba ta tabbatar wa jaridar
New Telegraph cewa shugabannin Boko Haram na gargadi ga mabiyansu.
“Daga
labaran liken asirin da muke samu.wasu yan Boko Haram sun shiga hannun
shugabanninsu, suna musu gargadi kada su gudu a filin fama ko a kashe
su,”
Hakazalika, Kwamandan Operationlafiya
dole,Manjo Janar Lucky Irabor, ya tabbatar da wannan barazanar da
shugabannin Boko Haram din keyi.
Kana, Lucky Irabor, yayi kira ga yan Boko Haram su mika kansu a yanzu da suke daman yin hakan.
Yace rundunar soji zata kula da su sosai kuma game da hakkin dan adam
BBC HAUSA-An kara kama wasu alkalai da laifin cin hanci a Najeriya
Hukumar
da ke sanya ido a fannin shari'ar Najeriya ta bukaci a kori wasu alkali
biyu daga aiki bisa zargin da ta yi musu na karbar hanci.
Wata
sanarwa da kakakin hukumar Soji Oye ya fitar ranar Juma'a ta bukaci a
kori mai shari'a Ugbo Ononogbo na babbar kotun jihar Abia, sannan a yi
wa mai shari'a Nasir Gummi na babbar kotun jihar Zamfara ritayar dole
ba tare da bata lokaci ba.
Mr Oye ya kara da cewa, "Hukumar da ke
sanya ido kan fannin shari'a karkashin jagorancin alkalin alkalai na
kasa mai shari'a Walter S. N. Onnoghen, a taron da ta yi na 80, ta nemi
gwamnan Abia ya kori Ugbo Ononogbo, yayin da ta yi kira ga gwamnan
Zamfara da ya yi wa mai shari'a Gummi ritayar dole saboda samunsu da cin
hanci."
Sai dai alkalan ba su ce komai a kan zargin da ake yi musu ba.
Hukumar
ta kuma gargadi wasu alkalai, cikin su har da D. O. Oluwayemi na
ma'aikatar shari'a ta jihar Lagos da mai shari'a M. A. Savage na babbar
kotun Lagos kan zargin aikata ba daidai ba.
A watannin baya bayan
nan dai bangaren shari'a na Najeriya na shan caccaka daga 'yan
Najeriya, musamman bisa zargin cin hanci da rashawa da ake yi wa
alkalai.
Tuni dai aka gurfanar da wasu alkalan a gaban kotu bayan
hukumar tsaro ta farin-kaya ta kai samame gidajensu, inda ta ce ta samu
makudan kudaden da ake zargin sun karba ta hanyar cin hanci.
VOA HAUSA-Kwastan na shirin kara harajin shigowa da motoci da kashi 100
Hukumar kwastam a Najeriya na shirin yin karin kudin haraji akan
motocin kawa da ake shigowa da su daga kasashen ketare, a cewar wata
majiya kwakwara.
Karin wanda ake shirin sanarwa zai kai kashi dari-bisa-dari akan
motocin kirar Jeep-jeep kamar yadda majiyar wacce ta nemi a sakaya
sunanta ta tabbatarwa Sashen Hausa na Muryar Amurka.
Wannan sabon mataki da hukumar ke shirin dauka na zuwa ne makwanni
biyu da sanar da shirin hana shiga da motoci ta kan iyakokin kasar.
Ana sa ran shirin na hana shiga da motoci zai fara aiki ne nan da daya ga watan Janairun shekara mai zuwa.
Hukumar kwastam din ta yi korafin cewa Najeriya na rasa makudan kudaden haraji idan ana shigar da motocin ta kan iyakokin kasar.
A makon da ya gabata Majalisar dokokin kasar ta bukaci a dakatar da
shirin, wanda ta ce zai jefa dumbin 'yan Najeriya cikin kangin rashin
aikin yi.
Kwatsam kuma sai ga wannan mataki na karin haraji kan motoci kirar Jeep da ake shirin sanarwa.
“Tsarin haraji ya na sa gwamnati ta samu kudi amma kuma ya na sa
mutane cikin tsanani.” In ji Malam Lawal Habib na kwalejin Fasaha ta
Kano.
Kokarin jin ta bakin hukumar ta kwastam dangane da wannan shiri ya cutura.
DW HAUSA-Zimbabuwe: Mugabe ya sake zama dan takara
Jam'iyyar ZANU-PF mai mulkin Zimbabuwe ta sake zaben
Shugaba Robert Mugabe a matsayin dan takara a zaben shugaban kasa na
shekara ta 2018.
Jam'iyyar ZANU-PF mai mulkin kasar Zimbabuwe a wannan Asabar ta sake
tsayar da Shugaba Robert Mugabe dan shekaru 92 da haihuwa a matsayin dan
takara a zaben shugaban kasa na shekara ta 2018. Dubban magoya bayan
jam'iyyar sun yi ta shewa suna jinjina wa shugaban wanda ya shafe
shekaru 36 kan madafun iko, tun da kasar ta samu 'yanci a shekarar 1980
daga Turawan mulkin mallaka na Birtaniya.
Haka na nuna Shugaba
Mugabe yana neman tsawaita mulkin da ya yi na tsawon shekaru 36. Yanzu
haka kasar ta Zimbabuwe tana fuskantar matsalolin tattalin arziki da
hauhawar tashin farashin kayayyaki abin da ya janyo watsi da kudin kasar
a shekara ta 2009, inda aka rungumi amfani da kundin kasashen ketare.
RFI HAUSA-ECOWAS ta bukaci Jammeh ya mika mulkin Gambia
Rikicin siyasar Gambia, bayan Yahya Jammeh ya ki amincewa da shan kayi a zaben shugabancin kasar da Adama Barrow ya lashe.
Shugabannin
sun bukaci haka ne a taron ECOWAS na 50 da suka gudanar a birnin Abuja
na Najeriya, in da suka mafi mayar da hankali kan rikicin siyasar
Gambia.
Tuni dai Jammeh ya shigar da kara a kotun koli don
kalubalantar sakamakon wanda ya amice da shi a farko kafin ya bijire
daga bisani.
A farkon makwannan ne dakarun Jammeh suka kwace hukumar zaben kasar, abin da ya janyo masa suka daga kasashen duniya.
LEADERSHIP HAUSA-BABBAN LABARI: Kasafin Kudin 2017: Damuwar ‘Yan Nijeriya Ta Zo Karshe — Buhari
Shugaba
Muhammadu Buhari ya gabatar da Kasafin Kudin shekarar 2017 a gaban
Majalisun Kasar nan biyu, watau ta Dattawa da takwarta ta Dokoki, inda
yake bukatar su sahale wa Gwamnatin Tarayya ta kashe Naira Tiriliyan
bakwai da digo ashirin da takwas (7.28) wajen gudanar ayyukan da al’umma
za ta amfana
karanta sauran labaran>>>
Assalamu alaikum, Editan LEADERSHIP Hausa mai farin jini, ka bani dama na yi kira ga gwamna Kashim...
(null)
Samu dukkanin shirye-shiryen RFI Siyasa da Al'adu da Wasanni da Labarai da dumi-duminsu na Afrika da Faransa da duniya.
Flash or unlock your phone at SENIORA TECH shop No.51 upstairs.OLUMBO shopping complex Ahmadu Bello way Birnin kebbi. 08062543120 http://...
Domin samun labaran wasanni kai tsaye daga club na kwallon kafa na turai