KANUN LABARAI DAGA JARIDU DA KAFAFEN LABARAI

NAIJ.COM-Boko haram za ta kashe yan kungiyar ta da suka gudu a fagen daga

Shugabannin Boko Haram sunyi arazanar kashe duk mambansu da ya gudu daga dajin Sambisa a yankin arewa maso gabas.
Wannan barazanar na zuwa ne bayan rundunar soji Najeriya na wura way an Boko Haram din wuta a dajin.
Wani dan banga a Damboa, mai suna Malam Abubakar Buba ta tabbatar wa jaridar New Telegraph cewa shugabannin Boko Haram na gargadi ga mabiyansu.
“Daga labaran liken asirin da muke samu.wasu yan Boko Haram sun shiga hannun shugabanninsu, suna musu gargadi kada su gudu a filin fama ko a kashe su,”
Hakazalika, Kwamandan Operationlafiya dole,Manjo Janar Lucky Irabor, ya tabbatar da wannan barazanar da shugabannin Boko Haram din keyi.
Kana, Lucky Irabor, yayi kira ga yan Boko Haram su mika kansu a yanzu da suke daman yin hakan.
Yace rundunar soji zata kula da su sosai kuma game da hakkin dan adam

BBC HAUSA-An kara kama wasu alkalai da laifin cin hanci a Najeriya

 

Hukumar da ke sanya ido a fannin shari'ar Najeriya ta bukaci a kori wasu alkali biyu daga aiki bisa zargin da ta yi musu na karbar hanci.
Wata sanarwa da kakakin hukumar Soji Oye ya fitar ranar Juma'a ta bukaci a kori mai shari'a Ugbo Ononogbo na babbar kotun jihar Abia, sannan a yi wa mai shari'a Nasir Gummi na babbar kotun jihar Zamfara ritayar dole ba tare da bata lokaci ba.
Mr Oye ya kara da cewa, "Hukumar da ke sanya ido kan fannin shari'a karkashin jagorancin alkalin alkalai na kasa mai shari'a Walter S. N. Onnoghen, a taron da ta yi na 80, ta nemi gwamnan Abia ya kori Ugbo Ononogbo, yayin da ta yi kira ga gwamnan Zamfara da ya yi wa mai shari'a Gummi ritayar dole saboda samunsu da cin hanci."
Sai dai alkalan ba su ce komai a kan zargin da ake yi musu ba.
Hukumar ta kuma gargadi wasu alkalai, cikin su har da D. O. Oluwayemi na ma'aikatar shari'a ta jihar Lagos da mai shari'a M. A. Savage na babbar kotun Lagos kan zargin aikata ba daidai ba.
A watannin baya bayan nan dai bangaren shari'a na Najeriya na shan caccaka daga 'yan Najeriya, musamman bisa zargin cin hanci da rashawa da ake yi wa alkalai.
Tuni dai aka gurfanar da wasu alkalan a gaban kotu bayan hukumar tsaro ta farin-kaya ta kai samame gidajensu, inda ta ce ta samu makudan kudaden da ake zargin sun karba ta hanyar cin hanci.

Gida - Leadership Hausa

Assalamu alaikum, Editan LEADERSHIP Hausa mai farin jini, ka bani dama na yi kira ga gwamna Kashim...

Gida

(null)

Labarai, kai tsaye- Radio France Internationale RFI

Samu dukkanin shirye-shiryen RFI Siyasa da Al'adu da Wasanni da Labarai da dumi-duminsu na Afrika da Faransa da duniya.

NIGERIAN NEWSPAPERS

Flash or unlock your phone at SENIORA TECH shop No.51 upstairs.OLUMBO shopping complex Ahmadu Bello way Birnin kebbi. 08062543120 http://...

Wasanni

Domin samun labaran wasanni kai tsaye daga club na kwallon kafa na turai

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN