Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari
ya ce sojojin kasar sun fatattaki mayakan kungiyar Boko Haram daga
babbar maboyarsu a dajin Sambisa.
A cikin wata sanarwa, shugaba Buhari ya ce yanzu mayakan kungiyar suna kan arcewa ne, kuma ba su da sauran wurin buya. A 'yan makonnin da suka gabata, sojojin Najeriya sun kaddamar da babban farmaki a dajin Sambisa, dake jihar Borno.
An yi ta baza jita-jita akan cewa mayakan kungiyar Boko Haram din na rike da wasu daga cikin 'yan matan Chibok ne a cikin dajin.
Wasu daga cikin 'yan matan da suka samu kubuta bayan an sace su, sun ce an ajiye su ne a cikin dajin.
Tun daga watan Fabrairu da sojojin Najeriyar suka kaddamar da wani sabon farmaki, sojojin sun kwato yankuna da dama da a baya kungiyar Boko Haram din ke iko da su.
BBC HAUSA
Gida - Leadership Hausa
Assalamu alaikum, Editan LEADERSHIP Hausa mai farin jini, ka bani dama na yi kira ga gwamna Kashim...
Gida
(null)
Labarai, kai tsaye- Radio France Internationale RFI
Samu dukkanin shirye-shiryen RFI Siyasa da Al'adu da Wasanni da Labarai da dumi-duminsu na Afrika da Faransa da duniya.
NIGERIAN NEWSPAPERS
Flash or unlock your phone at SENIORA TECH shop No.51 upstairs.OLUMBO shopping complex Ahmadu Bello way Birnin kebbi. 08062543120 http://...
Wasanni
Domin samun labaran wasanni kai tsaye daga club na kwallon kafa na turai
Tags:
LABARI