Sojoji sun kama kasurgumin kwamandan kungiyar Boko Haram a sansanin'yan gudun hijira


Hukumar sojin Najeriya ta bayyana cewar ta kama, Maje Lawan, kwamandan kungiyar Boko Haramda ta dade tana nema ruwa a jallo. 

A cewar darektan yada labarai na hukumar sojin Najeriya, Birgediya janar Texas Chukwu, Maje ne na 96 a jerin sunayen 'ya'yan kungiyar Boko Haram da hukumar ke nema ruwa a jallo. 

An kama shi ne a Banki dake jihar Borno. Chukwu ya bayyana cewar an kama Maje ne bayan ya yi basaja ya sumama cikin sansanin 'yan gudun hijira. 

Yanzu haka yana hannun hukumar ta soji domin amsa tambayoyi kafin mika shi ga hukumar da tafi cancanta. Kazalika Chukwu ya bayyana yadda rundunar soji tayi nasarar kashe wasu mayakan kungiyar Boko Haram biyu a kauyen Malari bayan kaddamar da wani harin kwanaton bauna a kan 'yan ta'addar. An samu wasu kekeunan hawa 10 tare da 'yan ta'addar.

A wani labarin mai nasaba da wannan, Chukwu ya bayyana cewar dakarun soji sun fatattaki wasu 'yan ta'adda daga maboyar su dake Gbamjimba-Akor dake karamar hukumar Guma ta jihar Benuwe.

Ya kara da cewar wasu daga cikin 'yan ta'addar su mutu, sai dai bai ambaci adadinsu ba. 

An samu babbar bindiga samfurin AK-47 guda daya da alburusai da kuma Baburan hawa 5.
 

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> whatsapp://chat?code=41x2TuRqdVQ9PrcrucqpTu
Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com
Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

Hausa.naij.ng
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN