Rashin Imani: Ya yi wa karamar yarinya fyade, ya harbeta da cutar kanjamau


Jami’an hukumar Yansandan jihar Gombe sun sanar da cafke wasu mutane su bakwai da suka kwashe tsawon lokaci suna yi ma wata karamar yarinya mai kimanin shekaru goma sha hudu fyade, inji rahoton jaridar Aminiya. Majiyar NAIJ.com ta ruwaito daga cikin mutanen da aka kama, akwai Hamza Musa wanda a garin lalata da yarinyar ya harbeta da cutar nan mai karya garkuwan jiki, watau sida ko ace mata Kanjamau, haka zalika binciken Asibiti ya nuna yarinyar na dauke da juna biyu.

Wannan lamari ya faru ne a unguwar Poli, dake cikin karamar hukumar Yamaltu Deba, acan ne aka tafka yarinyar nan wannan aika aika, inda take zuwa yawon talla, kamar yadda mahaifinta mai suna Malam Abdullahi ya tabbatar. Shi kuwa wannan mutumi da ake zargin harbar yarinyar da cutar Kanjamau, mai suna Hamza Musa an kama shi ne a ranar Litinin da ta gabata, a shagonsa dake kasuwar Kwadon, inda yake sayar da alawa.

Mahaifin yarinyar, Malam Abdullahi ya bayyana cewa bayan wani dan bincike da aka gudanar, sai ga shi an damko wuyar mutane bakwai, mutanen da bincike ya nuna suma sun yi lalata da wannan yarinyar a unguwar Poli.

Tuni dai Hamza ya amsa laifinsa, kuma har ma an bada belinsa, amma da zarar an kammala bincike za’a gurfanar dasu duk gaban kuliyan manta sabo, kamar yadda wani jami’in ma’aikatar walwala na jihar Gombe ya bayyana.
 

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> whatsapp://chat?code=41x2TuRqdVQ9PrcrucqpTu Latsa nan domin ka sauke Manhajarmu ISYAKU.APK https://docs.google.com/uc?export=download&id=0B7lmLLhGZSx5OTVENFlsTkllRTQ Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

Hausa.naij.ng
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN