Malaman dai sun yi taro ne na kaddamar da wani littafin da
shehin malami Farfesa Umar Labdo na jami'ar Maitama Sule dake garin Kano ya
rubuta game da akidun shi'a da kuma dabi'o'in su da ya bayyana a matsayin
marasa kyau kuma abun kyama.
NAIJ.com ta samu cewa shima babban sakataren kungiyar
Jama'atunnasrul Islam Dakta Khalid Aliyu Abubakar ya bayyana kungiyar a
matsayin abun kyama sannan kuma ya bukaci hadin kan jama'a domin ganin an kawo
karshen ta.
Daga karshe dai malaman sun yi ittifakin cewa da ilimi ne ta
kuma hanyar wayar ma da al'umma kai da irin litattafai makamantan wadan nan ne
za a iya kawo karshen na shi'a a yankin na arewa.
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> whatsapp://chat?code=41x2TuRqdVQ9PrcrucqpTu
Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com
Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira
Hausa.naij.ng
Tags:
LABARI