Zaben Ekiti: An cafke wasu mutum 5 suna raba wa jama'a kudi lokacin zabe

Yansanda sun damke akalla mutum 5 a Ado Ekiti bayan an yi zargin suna raba wa jama'a kudi lokacin zaben Gwamnan jihar Ekiti da ake yi ranar Asabar. An damke wadannan mutane ne a gaban wata Mazaba da ke makarantar Jonathan Memorial a unguwar Ajilosun na babban birnin jihar ta Ekiti. 

Tun farko dai wasu yan takarar kujerar gwamna a karkashin jam'iyyun Mega party da Accord party watau  Bisi Omoyeni da Abiodun Aluko, sun yi zargin cewa wasu jama'a na ba masu kada kuri'a kudi domin a sayi kuri'unsu.

Dan takarar kujerar Gwamna a karkashin jam'iyar Accord party Abiodun Aluko, ya yi zargin cewa jam'iyar APC tana ba masu kada kuri'a N5000 a bayyane, domin su kada ma dan takarar APC kuri'a, ya ce ita kuma PDP tana ba jama'a N4000, bayan N3000 da ta biya a asusun ajiya na ma'aikatan gwamnatin jihar Ekiti.
 
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/Lq4Z5kPck53Le3ibU9RUnY Latsa nan domin ka sauke Manhajarmu ISYAKU.APK https://docs.google.com/uc?export=download&id=0B7lmLLhGZSx5OTVENFlsTkllRTQ Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN