Kebbi: Yadda ruwa ya shafe gonaki a Saminaka da kewaye a karamar hukumar Shanga

Sani Musa Saminaka | Shanga L.G| 16-7-2018

Ruwan sama tamkar da bakin kwarya ranar Lahadi ya yi sanadin cikewar Gulbin garin Saminaka, Wawa, Ganwo, Raha da kuma Dugu a yankin karamar hukumar Shanga na jihar Kebbi. Wannan lamarin ya yi sanadin shafewar gonakin gero, Masara, Dawa, Shinkafa da sauran amfanin gona sakamakon ruwa da ya mamaye gonakin.

Haka zalika wakilinmu na garin Saminaka ya tabbatar mana cewa hatta wasu gonakin Ayaba sun bi ruwa. 

Wani dattijo mazauni garin Wawa, Malam Garba Layin Gehe, ya shaida mana cewa an taba samun irin wannan ibtila'i fiye da shekara goma da suka gabata a wannan gari.

Kawo yanzu dai babu labarin rushewar gidaje ko salwantar rayuwa, amma dimbin kayakin amfanin gona sun salwanta a wannan lamari.

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/Lq4Z5kPck53Le3ibU9RUnY Latsa nan domin ka sauke Manhajarmu ISYAKU.APK https://docs.google.com/uc?export=download&id=0B7lmLLhGZSx5OTVENFlsTkllRTQ Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN