Labarin da ke shigowa yanzu da dumi-dumi na nuna cewa bayan
rikice-rikice, zanga-zanga da fadan baki, shugaban majalisan dattawa, Bukola
Saraki, ya sanar da fitarsa daga jam'iyyar APC.
Shugaban majalisan ya yi wannan sanarwa ne da yammacin nan
ta shafin sada ra'ayi da zumuntarsa na Tuwita. A jawabin yace: " Ina son
sanar da yan Najeriya cewa bayan shawarwarin da nayi sosai, na yanke shawaran
fita daga jam'iyyar All Progressives Cogress APC." Wannan abi na faruwa ne
bayan wasu daruruwan matasa sun tafi zanga-zanga sakatariyan jam'iyyar APC da
ke babban birnin tarayya Abuja.
An fara samu baraka a jam'iyyar APC ne tun ranar Talatan da
ya gabata, 24 ga watan Yuli, 2018 inda yan majalisan dattawa akalla 15 suka
fita daga jam'iyyar APC da yan majalisan wakilar 35. Abin mamakin shine
Kakakin majalisan wakilai, Yakubu Dogara da shugaban majalisan, Bukola Saraki,
sun zauna a jam'iyyar. Masu sharhi sun bayyana cewa akwai wani kaidi da suke
shirin kullawa da wannan rashin fita da sukayi.
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> whatsapp://chat?code=41x2TuRqdVQ9PrcrucqpTu Latsa nan domin ka sauke Manhajarmu ISYAKU.APK https://docs.google.com/uc?export=download&id=0B7lmLLhGZSx5OTVENFlsTkllRTQ Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira
Hausa.naij.ng