Ana cigiyan 'yan uwan wannan bawan Allah, Malam Idrisa dan asalin garin Alfagai a jihar Kebbi

Ana cigiyar wannan bawan Allah da hotonsa ya bayyana a wannan labari mai suna Malam Idrisa. Ya ce shi dan garin Alfagai ne da ke Birnin kebbi a nan jihar Kebbi. An sami wannan mutum ne a gidan wani hamshakin Malamai a kasar Sudan mai suna Sheikh Sala wanda ke zaune a jihar Kasala na kasar Sydan.

Malam Idrisa ya bar gida Najeriya da niyyar zuwa aikin Hajji da kafa, jin cewa ana zuwa acewar sa yataso  ne daga garin Alfagai dake Birnin Kebbi a tarayyar Nigeria yau kusan shekara daya da wani abu, da niyyar zuwa aikin Hajji kamar yanda ya samu labarin cewa ana iya zuwa ta mota, to amma yace ya taho ne ba tare da sanin 'ya 'yan sa ko wani daga cikin 'yan uwan sa ba domin ya san ba zasu bar shi ya taho ba, wanda shi kuma babban burinsa kenan a rayuwa, ya gana da Dakin Allah.


Wannan bawan Allah ya ambaci wasu cikin yan uwansa kamar Sarkin Zabarmawan Lagos Alhaji Ibarahim da kuma 'ya'yansa da ke garin Alfagai kamar: Fatima da 'yan uwanta.

Sakamakon haka ake cigiya duk wanda Allah yasa yasan shi, ko kuma ya san wani cikin wayannan yan uwa nasa ko kuma yasan garin su daya, ya sanar da yan uwan sa cewa su tun-tubi wannan lamba: (+249918289955) domin samun cikakken labari da kuma inda za'a sameshi, Dafatan Allah yasa mu dace.

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/Lq4Z5kPck53Le3ibU9RUnY Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN