Kungiyar
Kasashen Musulmi ta OIC ta karba kiran shugaba Recep Tayyip ErdoÄŸan akan
gudanar da taron koli akan Qudus a birnin Istanbul, kimanin wakilai
daga kasashen Musulmi 40 ne suke halartar taron a yau Juma'a.
A
taron da shugaba Recep Tayyip ErdoÄŸan ya kira cikin gaggawa a kan
lamurkan dake faruwa a Falasdin ya samu halartar shugabanin kasashe 13,
Firaministoci 2, mataimakan shugabanin kasashe 3, mataimakan firaminista
12, ministocin harkokin waje 11 da kuma manyan jami'an harkokin waje na
kasashe da dama.
A
taron shugabanin kasashen da suka hada da na Iran Hasan
Ruhani, Afganistan; Asharif Gani, sarkin Jordan 2. Abdullah, Sudan Omer
el-Beshir, Gine Bissau Jose Mario Waz da kuma shugaban Gine Alpha
Gonde, Sarkin Qatar Sheik Temim bin Hamed Al Sani, Sarkin
Kuwait Sheik Sabah el-Ahmed el-Jabir es-Sabah, Shugaban
Moritanya Muhammed Walid Abdulaziz, shugaban Jamhoriyar Demokradiyyar
Cyprus ta Turkiyya Mustafa Akıncı, Pakistan Shahid Hakan Abbasi
da Kırgızistan Muhammed Kalıy Abılgaziyev sun samu halarta.
Haka
kuma mataimakin firministan Indonesiya Yusuf Kalla, mataimakin shugaban
kasar Gambiya Aja Fatoumatta Tambajang, mataimakin Jamhoriyar
Demokradiyar Cyprus ta Turkiyya Kudret Özersay, da kuma ministan
harkokin wajen kasar, mataimakin firaministan Somali Mehdi
Muhammed
Julid, Mataimakin firaministan Yaman Abdulmelik el-Mihlaf
suna wakiltar kasashen su.
Bugu
da kari a taron kolin Kungiyar Kasashen Musulmin firaministan kasar
Falasdin Rami el-Hamdallah da Babban Sakataren Kungiyar Kasashen
Musulmi Yusuf bin Ahmed el-Useymin sun halarci taron.
Sojojin
Isra'ila dai sun budewa Falasdinawa wuta a ranar litinin data gabata a
yayinda suke gudanar da zanga-zangar kalubalantar yunkurin Amurka na
mayarda ofishin jakadancinta ta kasar Isra'ila zuwa Qudus lamarin da ya
haifar da mutuwar Falsadinawa 62 da kuma raunana kusan dubu uku.
Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com
#TRT