Karamar hukumar Suru za ta fara ba matasa 1000 alawus na N5000 kowane wata

Shugaban karamar hukumar mulki ta Suru a jihar Kebbi Alh. Usman Maigandi ya ce karamar hukumar Suru za ta fara biyan matasa dubu daya 1000 alawus na naira dubu biyar N5000 kowane wata domin ta taimaka masu sakamakon rashin aiki.

Alh. Usman ya shai wa wakilin ofishin jakadancin Najeriya haka yayin da yake zanawa da shi ranar Talata a Suru.Ya ce wannan ya kunshi adadin Mata 400 da Maza 600 a fadin karamar hukumar mulki ta Suru.

Daga bisani ya kara da cewa Majalisar sa ta dauki nauyin biyan kudin magani ga musakai maras karfi a karamar hukumar.

Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN