Yadda yansandan bayar da hannu suka cakume wanda yace shi soja ne

Yan kwanakin baya ne a Oja Oba na Illorin babban birnin jihar Kwara wasu da ake kyautata zaton yansanda ne masu bayar da hannu a titi suka sami wata yar hatsaniya da ya kai su ga cakume kuma suka kudundume wani da ya yi ikirarin cewa shi soja ne amma baya sanye da kakin soja a lokacin da lamarin ya faru.

Majiyarmu ta ce babu wanda ya san musabbabin faruwar matsalar, amma dai yansandan sun jawo wanda ake zaton cewa ya aikata laifin tukin abun hawa yayin da suka yi kokarin tafiya da shi zuwa ofishinsu.

Wannan lamari ya jawo yar cinkoso sakamakon yadda jama'a suka yi dafifi domin ganin yadda za ta kasance.

Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN