Ka san abin da boko haram ta bukata kafin ta sako yan matan Dapchi ?

Shugaban hukumar DSS na Najeriya Lawal Musa Daura ya ce kungiyar boko haram ta bukaci a tsagaita buda wuta da sojin Najeriya ke yi masu babu kakkautawa, kuma a bisa wannan shiri kungiyar ta sako yan matan makarantar Dapchi da ta sace kimanin wata daya da ya gabata.

Lawal Daura ya shaida haka ne yayin da yake gabatar da yan matan ga shugaba Muhammadu Buhari a Fadar Aso da ke Abuja.

Idan baku manta ba, shugaban kungiyar ta boko haram ya yi Allah wadai kan irin yadda sojin Najeriya suka addabi yan kungiyar da hare-hare da wasu kafofin watsa labarai suka ambato shugaban na boko haram Abubakar shikau ya kira "bala'i daga sojin Najeriya".

Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN