Gwamna Abubakar Atiku Bagudu na jihar Kebbi ya bukaci al'ummar jihar Kebbi su kasance masu kula da ayyuka da Gwamnati ta yi masu domin ganin aikin ya yi karko saboda a dade ana amfana da ayyukan.
Gwamna Bagudu ya bayyana wannan bukata ne a wani ziyarar gani da ido akan aikin ruwan sha da ya kai a ruggar Fulani a Hutawa kusa da garin Birnin kebbi.
Gwamnatin Abubakar Atiku Bagud ta dukufa wajen samar da hanyoyi a birane da karkara a fadin jihar Kebbi hadi da ababen more rayuwa kamar su rijiyoyin burtsatse,ilimi da inganta kiwon lafiya.
Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com
Gwamna Bagudu ya bayyana wannan bukata ne a wani ziyarar gani da ido akan aikin ruwan sha da ya kai a ruggar Fulani a Hutawa kusa da garin Birnin kebbi.
Gwamnatin Abubakar Atiku Bagud ta dukufa wajen samar da hanyoyi a birane da karkara a fadin jihar Kebbi hadi da ababen more rayuwa kamar su rijiyoyin burtsatse,ilimi da inganta kiwon lafiya.
Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com