Hukumar hana fataucin bil'adama ta kasa tare da hadin guiwa da rudunar tsaro ta DSS sun kama mutum 11 da ake zargi da fataucin yara a sassa daban-daban a jihar Anambra.Wadanda aka kama sun hada da Mata 8 da Maza 3 wadanda aka ce sun shahara wajen satar yara a yankin yamma maso gabacin Najeriya har da Lagos da Abuja.
An ceto yara 3 wadanda shekarunsu ya kama daga wata 8 zuwa shekara 4 daga samamen jami'an. Daga cikin yaran da aka ceto har da yarinya yar shekara 2 da aka sato daga garin Lagos da wani yaro dan shekara 4 da aka sato daga Gudaba a babban birnin tarayya Abuja.
Har yanzu ba a gane iyayen yaro dan wata 8 da aka ceto ba yayin da Rosemary Okafor yar shekara 30 ta sayar da yaron ta guda daya cikin yaranta hudu a kan N350.000 wai tana son ta yi amfani da kudin ne domin ta biya wa sauran yaran 3 kudin makaranta.
Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com
An ceto yara 3 wadanda shekarunsu ya kama daga wata 8 zuwa shekara 4 daga samamen jami'an. Daga cikin yaran da aka ceto har da yarinya yar shekara 2 da aka sato daga garin Lagos da wani yaro dan shekara 4 da aka sato daga Gudaba a babban birnin tarayya Abuja.
Har yanzu ba a gane iyayen yaro dan wata 8 da aka ceto ba yayin da Rosemary Okafor yar shekara 30 ta sayar da yaron ta guda daya cikin yaranta hudu a kan N350.000 wai tana son ta yi amfani da kudin ne domin ta biya wa sauran yaran 3 kudin makaranta.
Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com
Tags:
LABARI