Yadda Pasto ya kashe wacce ya yi wa ciki domin gudun tonon asiri

Hukumar yansanda a jihar Rivers ta gabatar wa manema labarai wani Pasto mai suna  Pastor Chidiebere Okoroafor na Chochin Alter of Grace Ministries wanda take zargin ya kashe budurwarsa mai dauke da juna biyu tare da wasu mutum biyu a karamar hukumar Oyigbo .

Wadanda ake zargin cewa Paston ya kashe bayan budurwarsa da ya yi waciki sun hada da mata biyu masu dauke da jua biyu dukkansu tare da wata karamar yarinya .

Rahotanni sun nuna cewa Pastor Chidiebere ya yi wa budurwarsa ciki ne kuma ya bukaci ta zubar da cikin, amma sai ta ki ta aminta da bukatarsa ganin cewa ita mamba ce ta Chichinsa.Sakamakon haka Pasto ya kashe budurwar tasa mai suna  Olumma Onweagba kuma ya bizine ta a harabar Chochin.

Bayanai sun kara haske cewa su kuma matan guda biyu sun gamu da ajalinsu ne domin su ne suka san da zancen ciki da ya yi wa Olumma Onweagba, dukkannin wadaanda ake zargin Pasto ya kashe an bizine su ne a cikin harabar Chochin.

Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN