Rashin biyan kudi ya sa asibiti yin garkuwa da jaririya har tsawon wata 5

Wani Asibiti a gabacin kasar Gabon ya tsare wata jaririya har tsawon wata biyar sakamakon gazawar mahaifiyarta wajen biyan kudin Asibiti wanda ya kai CFA miliyan 2 watau dala 3.630.

Mahaifiyar jaririyar Sonia Okome ta kasance cikin farinciki bayan jama'a sun tara kudi suka biya bashin Asibitin mai zaman kansa daga bisani aka ba ta jaririyarta.

Bayanai sun nuna cewa zancen ya kai ga kunnen shugaban kasar ta Gabon Ali Bongo wanda shi ma ya bayar da nasa taimako.

Wata majiya ta labarta cewa hukumomi a kasar ta Gabon sun kama babban Likita na Asibitin bisa zargin sace jariri amma daga bisani aka yi watsi da wannan tuhumar.

Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN