Karamar hukumar Zuru za ta gina wa yan kasuwan Zuru ofis a cikin kasuwa

Shugaban karamar hukumar mulki ta Zuru a kudancin jihar Kebbi Alh. Muhammed Kabir Abubakar ya ce Majalisarsa za ta gina wa yan kasuwa ofis a sabuwar babban kasuwar garin Zuru hedikwatar Masarautar Zuru.

Alh.Kabir ya yi wannan bayanin ne a ofishin Mataimakin Gwamnan jihar Kebbi Alh. Samaila Yombe Dabai yayin da tawagar kungiyar 'yan kasuwar Zuru suka kai ziyara a ofishin Mataimakin Gwamna a Birnin kebbi ranar Laraba.

Ya ce za'a yi amfani da kudin shiga da karamar hukumar ke samu ne domin a gina ofishin domin su ma yan kasuwa su amfana da Gwamnati.

Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN