Kalli yadda miji ya daddatsa matarshi da adda kuma ya kashe kanshi

Wani mutum ya kashe kanshi bayan ya sassare matarshi da adda a jihar Delta. Matar mai suna Mr.Promise tana kwance a cibiyar kula da marasa lafiya na tarayya da ke Asaba inda take jinyar sara da mijinta ya yi mata da adda da yammacin ranar Litinin.

Wata majiya ta labarta cewa matar ta dawo daga tafiya ne da yammacin ranar, ba tare da sanin manufar mijinta ba daga shigar ta gida sai mijin ya fara saran ta da adda .

Ganin haka ya sa dansa ya yi kururuwa da ya sa makwabta suka kawo taimako kuma aka kira yansanda. Isar yansanda ke da wuya sai suka gan mutumin kwance a kasa babu rai.

Tuni dai aka kai gawarsa dakin ajiye gawa a wani Asibiti da ba'a fadi sunan sa ba.

Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN