An kama sojin bogi 2 da suka yi wa sojin gaske fashin mota


Rundunar 'yansanda a jihar Niger ta kama wasu sojan bogi guda biyu sanye da tufafin soja bayan sun yi wa wani sojin gaske Sgt. Usman Saidu fashi wanda ke aiki da rundunar tsaron lafiyar fadar shugaban kasa Asokoro a cikin Abuja.

Wata majiya ta cewa wadanda aka kama sun dade suna addabar mazauna unguwar Dutsen Zuma da Madalla na yankin Suleja a jihar Niger.


Wadanda aka kama su ne Peter Ali dan shekara 27 da Paul Isyaku dan shekara 23, an kama samarin guda biyu ne bayan sun yi wa sojan fashin motarsa kirar Honda Accord yayin da yake kan hanyarsa ta dawowa daga Abuja daga bisani matasan suka karbe masa motar da sauran ababen da ke ciki.

Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN