Uba da kishiya sun kulle yaro 'dan shekara 2 a kurkukun gida (Hotuna)

Wani mutum mai suna Mr Pius Happy da Matarsa Mrs Alice sun gufana a gaban wata Kotu a birnin Benin na jihar Edo bayan 'yansanda sun gabatar da su a gaban Kotu. Mr. Pius da kishiyar uwar yaron Alice sun ci zarafin yaron 'dan shekara 2 ta hanyar kulle shi a wani 'daki kamar kurkuku a cikin gidan inda yake bahaya kuma ya ci abinci a waje daya.

Makwabta ne suka tsegunta wa jami'an 'yansanda lamari da ke faruwa dangane da wannan yaro a gidan, sakamakon haka 'yansanda suka kama ma'auratan guda biyu kuma suka gurfanar da su a gaban Kotu.

Amma daga bisani sashen da ke kula da gurfanar da masu laifi na jihar DPP sun karbi ragamar shigar da karar daga hannun 'yansanda. Wani Lauya Barr. Adekunbi mai wakiltar ma'aikatar shari'a na jihar sashen DPP ya karbi ragamar.

A cewar Barr. Adekunbi ya yi haka ne sakamakon muhimmancin shari'ar domin a yi wa yaron adalci.

kalli bahaya kuma ga abinci a daki daya inda aka kulle yaron dan shekara 2






Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com *** GURBIN TALLA *** Kana son ka yi flashing ko ka cire makulli watau security na wayar ka? ka zo SENIORA TECH a OLUMBO PLAZA yamma da Gidan Wazirin Gwandu kan titin Ahmadu Bello a garin Birnin Kebbi. Shago Lamba 51 hawa na sama.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN