Labarai a yau Asabar 16/12/2017 (Safe)

Fitinan 'yan fashi da makami tare da yin garkuwa da mutane na cikin abubuwan da suka addabi yankin arewa maso yammacin Najeriya a tabarbarewar tsaron Najeriya.

Fashi da makami da garkuwa da mutane na haddasa asarar rayuka da dimbin miliyoyin Nera, musamman idan aka yi la'akari da zunzurutun kudaden da masu garkuwa da mutane ke amsa hannun 'yanuwan wadanda suka sace.

Gwamnan ya bayyana hanyar da aka gano miyagun mutanen na samun makamai. Ya ce wanda aka ga ya na da makamai da suka fi naka inganci sai a lallaba da hikima a san yadda za'a shawo kansa. A cewarsa idan mutum daya ya yi laifi sai a kamashi a kasheshi tare da kone wurin da yake. Daga bisani sai 'yanuwansa su tattaro da karfi su mamaye wurin su kashe duk wadanda su ke yankin. Injishi wannan halin jahilci ne na shekaru aru aru da suka wuce.
Muggan makaman, a cewar gwamna Yari suna fitowa ne daga kasashen Libya, Niger, Mali da makamantansu.


A dai dai lokacin da hankula ke kwantawa biyo bayan tashe tashen hankula da rikicin kabilancin da suka auku cikin kwanakin nan a wasu sassan jihar Adamawan, yanzu haka gwamnatin jihar ta umarci shugabanin da kuma masu fada aji,da su tashi tsaye wajen fadakar da al’umma muhammancin zaman lafiya.

A wata sanarwar da gwamnatin jihar ta fitar, Gwamnan jihar Senata Muhammadu Bindow Umaru Jibrilla yace dole yan jihar su yi karatun ta natsu ganin illar dake akwai a tashe tashen hankulan da suka auku cikin kwanakin nan,musamman a yankunan Numan da Demsa,wanda ke da nasaba da fadan kabilanci.

Gwamnan ta bakin hadiminsa ta fuskar harkokin yada labarai, Mr Martins Dickson yace gwamnati ba za ta kyale wasu dake daukar doka a hannunsu ba, yayin da ya yaba da kokarin da wasu suka soma na kawo fahimtar juna a cikin al’umma.

Wata Kotun soji da ke zaman ta a Maidugurin arewacin Najeriya ta yankewa wani soja hukuncin kisa saboda samun sa da laifin kashe fararen hula.
A wata sanarwar da ta fitar, Kakakin Sojin Najeriya Kinsley Mfon Samuel, ya ce Sojan mai igiya daya John Godwin ya harbe fararen hula 5 da aka kubutar a garin Yamteke da ke jihar Borno kuma ake bincike akan su.

Sanarwar ta kuma ce akwai wasu sojoji da aka yankewa hukuncin daurin rai-da-rai kan laifukan da suka shafi kisa da samun makamai da haramtacciyar hanya.

Sojojin sun hada da Innocent Ototo mai igiya biyu da aka samu da azabtarwa tare da kisan wani yaro mai shekaru 13 da ya ce ya sace masa wayar hannu, a unguwar Zamanbari da ke Maiduguri.

Shi kuma Benjamin Osage mai igiya daya da Sunday Onwe mara igiya an yanke musu hukuncin zaman gidan yari na shekaru 20 kan samun makamai ta haramtacciyar hanya.

Ko a watan Yuni da ya gabata an taba yankewa wani soja hukuncin kisa kan kashe wani da ake zargi dan Boko Haram ne.

Kungiyar kare hakkin bil’adama ta Human Right Watch ta sha zargin Sojojin Najeriya da cin zarafin fararen hula a Rikicin Boko Haram.

HRW ta ce ana garkame da duban mutane na tsawon lokaci ba tare da hukunci ko binciken zargin da ake musu na alaka da Boko Haram ba.

Kaddamar da yakin Boko Haram ya yi sanadi rayuka akalla 20,000 daga shekara ta 2009.

An hana wata 'yar Najeriya da ta kammala karatun lauya zama lauya - mai iya aiki a kotu - saboda hijabin da ta saka wanda ake ganin ya saba wa dokar tufafin makarantar horars da lauyoyin kasar.

Shugaban makarantar horas da lauyoyi Isa Hayatu Chiroma ya shaida wa BBC cewa an hana Amasa Firdaus shiga dakin taron yaye lauyoyi ne saboda bata sanya tufafin da ya dace ba.

Ta ki ta cire hijabinta, tana mai cewa dole ta saka hular lauyoyi kan dan-kwalinta, in ji shafin intanet na Nigerianlawyer.com.
Rahotanni sun ce Firdaus ta bayyana matakin a matsayin wani abin da ya keta hakkinta na bil Adama.

Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com *** GURBIN TALLA *** Kana son ka yi flashing ko ka cire makulli watau security na wayar ka? ka zo SENIORA TECH a OLUMBO PLAZA yamma da Gidan Wazirin Gwandu kan titin Ahmadu Bello a garin Birnin Kebbi. Shago Lamba 51 hawa na sama.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN