Jita-jitan karin kudin man fetur ba gaskiya bane - NNPC

An kula da samun dogon layi na masu son sayen man fetur a gidajen mai na Najeriya musamman a jihar Lagos da sauran sassan Najeriya sakamakon jita-jita da ake yadawa cewa za'a kara kudin litar man fetur.

Amma a wata sanarwa da kanfanin man fetur na kasa NNPC ya fitar ya musanta wannan jita-jitan, sanarwar ta ce har yanzu farashin litar man fetur a kasa yana nan akan N145 a kowane lita kuma kamfanin na da isashshen man fetur da zai wadatar da masu ababen hawa lokacin bukukuwan karshen shekara.

An kula da dogayen layi na masu son sayen man fetur a gidajen mai a garin Lagos tun karfe 4:30 na safe. Wasu giddajen mai suna sayar da mai yayin da wasu kuma suka ce basu da mai a ma'adanin su na mai.
 
**************************************** Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com **************************************** Kana son ka yi flashing ko ka cire makulli watau security na wayar ka? ka zo SENIORA TECH a OLUMBO PLAZA yamma da Gidan Wazirin Gwandu kan titin Ahmadu Bello a garin Birnin Kebbi. Shago Lamba 51 hawa na sama.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN