Wajibi ne soji su koyi harshen Hausa,Igbo,Yoruba kafin Disamba 2018

Rundunar Sojin Najeriya ta ba jami'an ta umarni domin su koyi harsunan Hausa, Igbo, da Yoruba kafin karshen watan Disamba na 2018. Sanarwar haka ya fito ne daga hannun mai hulda da jama'a da harkokin labarai na rundunar Gen.Sani Kukasheka .

Kukasheka ya ce iya wadannan yaren zai taimaka wa jami'an domin tafiyar da aikin su kamar yadda ya kamata.

Ya ce rundunar Soji ta fito da wannan tsari ne domin inganta hulda tsakanin jami'an ta da 'yan Najeriya haka zalika tsakanin ma'aikatan kaki da samun sauki wajen mu'amala a tsakanin Sojin su kansu.

Ya kara da cewa duk da yake harshen Turanci shi ne yare na bai daya a Najeriya amma iya sauran manyan yare da harsunan Najeriya zai kasance da muhimmancin gaske.

Kafin wannan lakacin rundunar da bukaci jami'anta su koyi harsunan French, Arabic da Spanish domin su iya fuskantar kalubale na hulda idan aka tura su aikin Majalisar Dinkin Duniya ko gudanar da harkar yau da kullum .


Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN