Sama da mutum 50 ne aka kashe 'yan kwanakin baya a karamar hukumar Shinkafi wanda ake zargin cewa barayi ne suka aikata wannan aikin, hakan ya kara zafafa zaman zullumi da ake yi a fadin jihar ganin cewa matsalar kisan mai-uwa-da -wabi ya sake dawowa a wasu yankuna na jihar Zamfara.
Mai taimaka wa gwamnan jihar Zamfara kan sha’anin tsaro Ibrahim Dosara ya ce ba gaskiya ba ne kalaman da ake cewa gwamnatin jihar tana sakaci a kan al’amarin.
Ya ce matsalar tsaro al’amari ne da ya shafi yankuna daban-daban na cikin kasa, kuma gwamnatin jihar a nata bangaren tana iyakar bakin kokarinta wajen ganin ta shawo kan matsalar.
Wata kungiya mai karajin kare hakkin bil'adama ta yi barazana cewa za ta maka Gwamnatin Zamfara a Kotu bisa zatgin gazawar Gwamnati wajen kare rayukan al'ummar jihar.
Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com
Mai taimaka wa gwamnan jihar Zamfara kan sha’anin tsaro Ibrahim Dosara ya ce ba gaskiya ba ne kalaman da ake cewa gwamnatin jihar tana sakaci a kan al’amarin.
Ya ce matsalar tsaro al’amari ne da ya shafi yankuna daban-daban na cikin kasa, kuma gwamnatin jihar a nata bangaren tana iyakar bakin kokarinta wajen ganin ta shawo kan matsalar.
Wata kungiya mai karajin kare hakkin bil'adama ta yi barazana cewa za ta maka Gwamnatin Zamfara a Kotu bisa zatgin gazawar Gwamnati wajen kare rayukan al'ummar jihar.
Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com
Tags:
LABARI