Daga Nura Bena, Isyaku Garba |
Mai girma Mataimakin Gwamnan jihar kebbi Alh. Samaila Yombe
Dabai ya yi kira ga al'ummar Masarautar Zuru da su ci gaba da mara wa Gwamnatin jiha baya akan shirye shirye da manufofinta domin Kara
samar wa jama'ar yankin karin ayukkan ci gaba.
Alh. Samaila yombe Dabai yayi wannan kiran ne a lokacin da
yake lale marhaban da manyan 'Yan siyasa da masu hannu da tsaki a
sha'anin siyasar yankin na masarautar ta Zuru da kewaye a ofishin sa.
Ya ce ya nuna jagoranci nagari a Karkashin jamiyyar APC chanji. Musamman idan a kayi la'akari da bada Mukaman SSA watau masu baiwa Gwamna shawara na musamman, da dai saurasu.
Alh. Samailia Yombe Dabai ya jadda da kudurin Gwamnatin jiha na kawo karin ababen more rayuwa ga al'ummar jihar nan da ma kasa baki daya
Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com