Nura Bena Daga Gidan Gwamnati |
Mataimakin Gwamnan jihar Kebbi Alh. Samaila Yombe Dabai ya kai ziyara a babbar Asibitin jiha dake Kalgo ranar Talata domin duba yadda aikin kula da samar wa jama'a lafiya ke gudana ,bisa ga kokarin da Gwamnatin jiha da take yi a halin yanzu haka.
Mataimakin Gwamnan jihar Kebbi Alh. Samaila Yombe Dabai ya kai ziyara a babbar Asibitin jiha dake Kalgo ranar Talata domin duba yadda aikin kula da samar wa jama'a lafiya ke gudana ,bisa ga kokarin da Gwamnatin jiha da take yi a halin yanzu haka.
A lokacin ziyar ta Mataimakin Gwamnan ya zagaya wurare
daban daban a cikin Asibitin, tare da nuna gamsuwar sa akan yadda aikin ke
tafiya.
Alh. Samaila Yombe Dabai ya yi kira ga jama'ar da ke wurin da su kara hakuri tare da basu tabbacin cewa duk wadan da aka tantance za a duba shi kamar yadda aka tsara.
Alh. Samaila Yombe Dabai ya yi kira ga jama'ar da ke wurin da su kara hakuri tare da basu tabbacin cewa duk wadan da aka tantance za a duba shi kamar yadda aka tsara.
Haka Kuma ya yaba tare da jinjina wa Likitocin hadi da ma aikatan da ke kula da Sha anin aikin .
Mataimakin Gwamnan Alh. Samaila Yombe Dabai ya ce Gwamnan
jiha Sanata Abubakar Atiku Bagudu ya chanchanchi a yaba mishi bisa irin namijin kokarin da yake yi a fanni daban baban musamman a sha'anin kiyon
lafiya, noma ,ilimi da sauransu.
Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com