Gwamna Atiku Bagudu ya dukufa wajen inganta lafiyar al'umma - Samaila Yombe

Nura Bena Daga Gidan Gwamnati |

Mataimakin Gwamnan jihar Kebbi Alh. Samaila Yombe Dabai ya kai ziyara a babbar Asibitin jiha dake Kalgo ranar Talata domin duba yadda aikin kula da samar wa  jama'a lafiya ke gudana ,bisa ga kokarin da Gwamnatin jiha da take yi a halin yanzu haka.

A lokacin ziyar ta Mataimakin Gwamnan ya zagaya wurare daban daban a cikin Asibitin, tare da nuna gamsuwar sa akan yadda aikin ke tafiya.

Alh. Samaila Yombe Dabai ya yi kira ga jama'ar da ke wurin da su kara hakuri tare da basu tabbacin cewa duk wadan da aka tantance za a duba shi kamar yadda aka tsara. 


Haka Kuma ya yaba tare da jinjina wa Likitocin hadi da ma aikatan da ke kula da Sha anin aikin .

Mataimakin Gwamnan Alh. Samaila Yombe Dabai ya ce Gwamnan jiha Sanata Abubakar Atiku Bagudu ya chanchanchi a yaba mishi bisa irin namijin kokarin da yake yi a fanni daban baban musamman a sha'anin kiyon lafiya, noma ,ilimi da sauransu.


Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN