Sheikh Isa Pantami wanda shine shugaban hukumar bunkasa fasahar sadarwa ta kasa (NITDA) ya musanta zance da wasu ke yi cewa hukumar EFCC tana bincikensa.
Wannan ya biyo bayan wadansu
rahotanni da ba a tabbatar ba sun ruwaito Ministan Sadarwar kasar
Adebayo Shittu yana cewa gwamnatin tarayya tana jiran sakamakon wani
binciken da hukumar EFCC take wa shugabannin hukumar NITDA.
Ya ce hukumar EFCC ba ta taba bincikarsa ba ko wani ma'aikacinsa tun da ya kama aiki da hukumar NITDA.
"EFCC sanya mana albarka take game da kokarin da muke na kawo gyara a hukumar NITDA," kamar yadda ya ce.
Tags:
LABARI