Malamin Nursery ya yi wa 'yar shekara 2 fyade

Ana zargin wani Malamin Makaranta wanda ke koyar da ajin 'yan Nursery da yi wa wata yarinya 'yar shekara biyu fyade a Orlu na jihar Imo ranar Laraba.

Bayanai sun nuna cewa an gabatar da wanda ake tuhuma gaban 'yansanda ,lamarin da ya  sa 'yan uwansa suka shaida wa jami'an 'yansanda cewa wanda ake zargin yana da tabin hankali.

Wata majiya ta labarta mana cewa wadanda suka kai karan Malamin basu gamsu da bayanin 'yan uwan wanda ake zargi ba bisa hujjar cewa babu yadda za'ayi a dauki Mahaukaci aikin koyarwa na Malamta.

'Yansanda na ci gaba da bincike kan lamarin bayan Likita ya duba yarinyar ya kuma bukaci a dawo da ita bayan wata daya domin ayi mata gwajin cutar HIV.

Ga masu shawara,aiko labari ko korafi ku rubuto zuwa isyakulabari@gmail.com Kaunace mu a Facebook https://www.facebook.com/isyakuweb Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN