Lugudin wutan jiragen yakin sojin Najeriya ya kashe matar Abubakar Shikau

Ana kyautata zaton cewa an kashe Uwargidan shugaban kungiyar boko haram Malama Fitdasi a wani harin jiragen sama na Sojin sama na Najeriya a Daurawa  na kauyen Urga kusa da garin Konduga a jihar Borno.

Mai magana da yawun rundunar sojin sama na Najeriya Olatokunbo Adesanya ya ce ana kyautata zaton cewa Malama Fitdasi tana wakiltar Maigidan ta ne Abubakar Shikau a wani taro na sirri da aka shirya wadda ya sami halarcin wasu 'yayan kungiyar ta BH kafin a kai hari a wajen da suke taron..

Hakan ya faru kasa da mako daya bayan jiragen yakin sojin sama na Najeriya sun yi lugudin wuta akan 'yan kungiyar ta BH lamarin da ya kashe tare da jikata da dama a cikin su a kauyen Daurawa.


Ga masu shawara,aiko labari ko korafi ku rubuto zuwa isyakulabari@gmail.com Kaunace mu a Facebook https://www.facebook.com/isyakuweb Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN