A kokarin gwamnatin jiha na ingata Samar da kiyon lafiya ga
daukacin jama'ar jihar Kebbi kyauta wata tawagar kwararrun
likitoci sun sauka a jihar nan , a cikin su kuwa har da Diyar mai-girma
mataimakin gwamnan jiha Watau Dr. Zainab Samaila Yombe Dabai wadda ita ma Likita ce , ta bayyana cewa ta zo ne gida domin ita ma ta bada na ta gudunmawa domin kishin gida
da kuma ganin irin kokarin Gwamnatin Sanata Abubakar Atiku Bagudu ta keyi ga al'ummar jihar nan musamman ga talakawa na ganin ta cimma
gurin ta a fanin kiyon lafiya ga ilahirin jama'ar jihar Kebbi.
Tawagar likitoci su samu tarbo da marhabin lale daga Mataimakin Gwamnan jihar Kebbi Col.Samaila Yombe Dabai MNI, tare da Babbar sakatareya ta
ma aikatar lifiya Hajiya Halima Boyi Dikko,da Dr.Aminu Bunza hadi da
sauran Yan kwamitin da ke gudanar da aikin kula da Sha anin a halin
yanzu haka da akeyi a babbar Asibirin na Kalgo.
Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com