Zargi: Kotu ta garkame Ma'aikaci a gidan Yari bisa zagin Gwamna Dankwambo

Kotu ta adana wani mutum a gidan Yari mai suna Abubakar Adamu dan shekara 35 kuma Ma'aikaci a  karkashin Gwamnatin jihar Gombe bisa zarginsa da zagin Gwamnan jihar Gombe Gwamna Dankwambo da Mahaifiyarsa.

Shi dai Abubakar Adamu yana aiki da Ma'aikatar kula da sha'anin ilimi mai zurfi na jihar Gombe kafin ya bayyana a gaban Kotu sakamakon kara da wani mai suna Inuwa Dattijo da ake wa lakabi da DJ Maitaya ya shigar a gaban Kotu inda yake zargin cewa shi Abubakar Adamu ya zage Gwamnan a wani faifen murya da ya aiko masa.

Dan sanda mai gabatar da kara Inspector Habibu Danjuma ya shaida wa Kotun cewa wadda ake karan ya gaza yin bayani mai gamsarwa akan wanda ya aiko masa sakon, a cewarsa wannan ya saba wa sashe na 156 na Penal Code.

An dage shara'ar zuwa ranar 26 ga watan Satumba 2017.

Kaunace mu a Facebook https://www.facebook.com/isyakuweb Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN