Dan Luwadi ya kashe Saurayi domin yana soyayya da Yarinya

Labarai da ke fitowa daga birnin Abuja sun nuna cewa wani sanannen dan Luwadi mai suna Samarola Musa ya kashe wani yaro da ke koyon aiki a shagonsa wadda kuma ya batashi ta hanyar tilasta shi yin luwadi da shi a garin Lugbe na babban birnin tarayya Abuja.

Lamarin ya faru ne bayan shi Musa dan Luwadi ya kama yaron nasa mai suna Ademola Adeshina yana zina da wata yarinya lamarin da ya harzuka Musa ya rufe Ademola da duka daga bisani kuma ya mutu.

Punch Metro ta ruwaito cewa Musa ya shaida wa mahaifin yaron cewa Ademola ya mutu ne sakamakon cutar Malaria, amma yarinyar da ta shaida abin da ya faru ta musanta wa Mahaifin Ademola. Sakamakon haka  Mahaifin ya shaida wa 'yan sanda kuma ya bukaci a gudanar da bincike akan gawar.

Daga bisani sakamakon bincken ya nuna cewa Musa yana yi wa Ademola Luwadi kuma an tabbatar da raunuka a cikin jikinsa da zasu iya zama musabbabin mutuwarsa.

Kotu ta adana wadda ake zargin a gidan Yari har zuwa ranar Litinin 20 ga watan Nuwamba 2017.



Kaunace mu a Facebook https://www.facebook.com/isyakuweb Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN