Bullar cutar amai da gudawa ya kashe mutum 20 a jihar Kebbi

Mutum 20 sun mutu sakamakon bullar cutar amai da gudawa a jihar Kebbi a lamari da ya fi kamari a kananan hukumomin  Shanga, Birnin Kebbi, Fakai da Koko/Besse.

Haka zalika cutar ta shafi mazauna  Tungar Buzu, Korama,  Samanaji da Keri a karamar hukumar Shanga lamarinda tuni ya haifar da fargaba a garin Tungar Buzu da kewaye kamar yadda wani mazunin Tungar Buzu Abdullahi Usman ya shaida wa Daily Trust.

Bayanai sun nuna cewa Gwamnatin jihar Kebbi tana sane da lamarin kuma tuni ta tura magunguna,kayan agaji da kwararru zuwa yankin da lamarin ya shafa domin a shawo kan cutar daga ci gaba da yaduwa.

 


Shafin mu na Facebook https://www.facebook.com/isyakuweb Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN