Birnin kebbi - Yadda tarbon Osinbajo ya shafi 'yan makaranta

 Isyaku Garba - Birnin kebbi

A bisa tsarin shirin tarbon mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo a ziyararsa zuwa jihar Kebbi,jera yara 'yan makaranta na cikin shirin wanda hakan yasa aka jera dalibai 'yan makaranta a kan wasu manyan tituna a cikin garin Birnin kebbi tun karfe 8:30 na safe har zuwa yanzu suna nan a jere akan wadannan tituna.

Wani yaro mai suna Ahmadu wadda yace shi dalibi ne a makarantar sakandare na Nagari da ke cikin Birnin kebbi ya tabbata mana cewa shi dai rana ce ta dame shi kuma yana fama da kishin ruwa.

Haka lamarin yake a wasu hanyoyi da ake kyautata zaton mataimakin shugaban kasa zai bi.

A ci gaba da zagayawa da muka yi a cikin garin Birnin kebbi wadda ke dauke da jami'an tsaro a gurare masu mahimmanci ,jama'a na ci gaba da gudanar da ayyukansu kamar yadda suka saba a kullum face kasancewar dalibai da jami'an tsaron a titunan Birnin kebbi da zai lurar da mutum cewa za'a sami babban bako a Birnin kebbi.



 
Ku biyo mu a
https://www.facebook.com/isyakuweb
Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a Whatsapp zuwa 08062543120.
Don aiko Labari ko korafi ka tuntube mu a 08062543120.
Shiga www.isyaku.com Don samun cikakken shafinmu da ke dauke da ababe masu kayatarwa.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN