Shugaba Muhammadu Buhari ya tattauna da Gwamna Willie Obiano na jihar Anambra ta wayan tarho inda ya jajanta masa tare da jama'ar jihar Anambra akan kisan gilla da wasu da ba'a san ko su waye ba suka kai a wani Choci inda harin ya halaka mutane da dama wasu kuma suka jikata.
A wani bayani da ya fito daga hannun mai taimaka wa shugaban kasa kan harkar jarida da hulda da jama'a Garba Shehu yace"Shugaba Buhari ya tausayawa wadanda lamarin ya rutsa da su kuma wannan ya nuna irin rashin imani da salo wadda wasu suka dauka domin suyi fada da zaman lafiyan 'yan Najeriya wadda Gwamnatinsa ba zata lamunta ba".
Shugaba Buhari ya tabbatar wa 'yan Najeriya cewa Gwamnatinsa zata yi iya kokarinta domin ta tabbatar da mutunci da lafiyarsu.
Ku biyo mu a
https://www.facebook.com/isyakuweb
Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a Whatsapp zuwa 08062543120.
Don aiko Labari ko korafi ka tuntube mu a 08062543120.
Shiga www.isyaku.com Don samun cikakken shafinmu da ke dauke da ababe masu kayatarwa.
A wani bayani da ya fito daga hannun mai taimaka wa shugaban kasa kan harkar jarida da hulda da jama'a Garba Shehu yace"Shugaba Buhari ya tausayawa wadanda lamarin ya rutsa da su kuma wannan ya nuna irin rashin imani da salo wadda wasu suka dauka domin suyi fada da zaman lafiyan 'yan Najeriya wadda Gwamnatinsa ba zata lamunta ba".
Shugaba Buhari ya tabbatar wa 'yan Najeriya cewa Gwamnatinsa zata yi iya kokarinta domin ta tabbatar da mutunci da lafiyarsu.
Ku biyo mu a
https://www.facebook.com/isyakuweb
Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a Whatsapp zuwa 08062543120.
Don aiko Labari ko korafi ka tuntube mu a 08062543120.
Shiga www.isyaku.com Don samun cikakken shafinmu da ke dauke da ababe masu kayatarwa.
Tags:
LABARI