Kakakin Majalisar dokoki a jihar Kogi yayi murabus

 Isyaku Garba - Birnin kebbi

Kakakin majalisar dokoki na jihar  Kogi  Umar Ahmed Iman yayi murabus kwana daya bayan majalisar ta dage zamanta sakamakon takaddamar da ta taso a cikin majalisar.

Magatakardar majalisar ne ya karanta wa 'yan majalisar takardar murabus da kakakin ya yi abinda ya kaiga kada kuri'ar da ya kai ga zaben Homourable Kolawole a matsayin sabon kakakin majalisar dokokin wanda dan gaban goshin Gwamna Yahaya Bello ne na jihar ta Kogi.

Bayanai sun nuna cewa takaddamar ta taso ne ranar Talata bisa cece-kuce a kan zancen cire shugaban masu rinjaye na majalisar wanda hakan ya rikide zuwa mataki da majalisar ta sami kanta a yanzu.




Ku biyo mu a
https://www.facebook.com/isyakuweb
Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a Whatsapp zuwa 08062543120.
Don aiko Labari ko korafi ka tuntube mu a 08062543120.
Shiga www.isyaku.com Don samun cikakken shafinmu da ke dauke da ababe masu kayatarwa.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN