Igbo na Najeriya basa da asali da Yahudawan Isra'ila - Sakamakon DNA

Tunani da fatan shugaban kungiyar al'umman Igbo wadanda ke alakanta asalin kabilar Igbo da kasancewa Yahudawa na kasar Isra'ila  (Re­deemed Israel Commu­nity of Nazarene Association RICON) ya gamu da cikas wanda ya biyo bayan sakamakon wani gwaji da aka fitar wadda ya nuna cewa ba abinda ya alakanta kabilar Igbo na Najeriya da Yahudun kasar Isra'ila.

Shugaban kungiyar muryar Yahudawa na Duniya (The international President of Jewish Voice Ministries) Rab­bi Jonathan Bernis shine ya bayar da sanarwar haka  a Uruagu-Nnewia yayin da yake gabatar da sakamakon gwajin da aka yi a dakin gwaje gwaje na kwayoyin halitta na DNA (Deoxyribonucleic acid) a garin Houston na kasar Amurka.

An karbi miyau daga Igbo 124 daga al'umma daban daban a Nnewi na jihar Anambara saboda a gudanar da gwajin na Y25,DNA a ranar 6 da 7 na Fabrairun 2017.



Ku biyo mu a
https://www.facebook.com/isyakuweb
Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a Whatsapp zuwa 08062543120.
Don aiko Labari ko korafi ka tuntube mu a 08062543120.
Shiga www.isyaku.com Don samun cikakken shafinmu da ke dauke da ababe masu kayatarwa.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN