kasar Nyanmar Ta ce ba za ta taba karban
bakwacin mambobin majalisar dinkin duniya a kasarsu wadanda aka turo
domin su yi bicinke game da kisan kiyashin da ake yiwa Musulman kasar.
Kakakin
gwamnatin kasar Nyanmar kana ministan harkokin waje ‘yar siyasa San Suu
Kyi wacce aka yi wa kyautar lambar yabo ta Nobel a fannin samar da
zaman lafiya. ta ce babu wanda ya isa ya bincike su game da halin da
Musulman Rohingya suke ciki, domin a cikin yarjejeniyar suka rattaba wa
hannu a watan Maris din da ya gabata ba’a taba batun za’a aiko musu da
tawagar hukumar kare hakki dan adam ta duniya ba.
A
nasa gefen, magatakardan ministan harkokin waje ta kasar Nyanmar Kyaw
Zeya cewa yayi : bamu ga abinda zai sa mu baiwa majalisar dinkin damar
yi mana shishshigi ba.Domin mu a kasarmu ma, mun tanadi kwararrun masu
bincike wadanda duniya ta amince da su.
Milyoyin
mutane daga sassa daban-daban na duniya na ci gaba da yin sukar Malama
Suu Kyi da kakkausar murya sabili da irin halin ko-in-kula da ta nuna a
lokacin da sojojin kasarta suka ci zalin sama da Musulman Rohingya
milyan 1 a Dakhine dake a yammacin kasar.
Ana
kyautata zaton kusan Musulman Rohingya dubu 7 da dari 5 ne suka guje wa
muhallansu domin neman mafaka a kasahen Bangaladash da Ä°ndiya.
Ku biyo mu a shafin mu na Facebook @isyakuweb https://web.facebook.com/isyakuweb Kana sha'awar ka sami labaranmu ta Whatsapp ? ka rubuto YES a Whatsapp zuwa 08062543120 zamu aiko maka da Labaran mu kai tsaye kyauta a koda yaushe muka wallafa Labari. Kana da sha'awar taimaka mana da Labarai, ko sharhi ? ka kira mu a 08062543120. Shiga shafinmu kai tsaye domin samun cikakkun Labarai.Ka shiga www.isyaku.com a browser ko opera ko firefox ko safari na wayarka zaka sami cikakken shafinmu da ke dauke da ababe masu kayatarwa.
Nyanmar: Babu wanda ya isa ya bincike mu game da Musulman Rohingya ya fara bayyana ne a shafin trt.
Tags:
DUNIYA