Nasihohi 35 da zasu taimakeka wurin samun ingantacciyar rayuwa | isyaku.com

1- ka fara yininka da sallar asubahi da azkar domin samun rabo da tsira.
2- ka zarce da istgfari har sai shaidan ya debe
tsammanin samun rabo a jikinka.
3-kar ka daina addu'a dumin itace igiyar tsira
4-ka tuna cewa mala'iku suna rubuta maganganunka.
5-kyawun yatsu shine ka rika qidaya TASBIH dasu.
6- idan ka shiga damuwa da qunci kace" la ila ha illallah".
7- ka sayi addu'ar talakawa da soyayyan marayu da kudadenka.
8-doguwar sujada 1 wanda aka yita saboda tsoron ALLAH yafi maka bene da aka gina na zinari.
9- ka tauna magana kafin kafadeta domin tana iya zama ajalinka.
10- ka guji addu'ar wanda aka zalunta da hawayen wanda aka hana.
11- kafin ka karanta jaridu da mujallu mai zai hana.kafara karanta alqur'ani.
12- ka zama dalilin gyaruwan iyalanka.
13- ka tilastawa ranka wurin bin dokokin Allah ,
domin ita rai tana umarni ne da sabon Allah.
14- kafin tsufar iyayanka ka daure ka samu yardarsu.
15-tsoffin tufafinka sababbi ne a wurin talakawa.
16- kar kayi fushi , domin rayuwa kadan ce ba kamar yadda kake tsammani ba.
17- tare dakai akwai wanda yafi kowa qarfi yafi kowa wadata, shine Allah.
18- kar ka rufe qofar tuba saboda sabon Allah.
19- sallah itace mafi alkhairin abun da zata taimakeka akan musibu da wahalhalu.
20- ka nisanci munanan zato, zaka huta kuma zaka hutar.
21- dalilin kowane damuwa juyawa Allah bayane, ka juyo zuwa gareshi mana.
22-kayi sallah irin wacce kakeso a shigar dakai qabari tare da ita.
23- idan kaji wanda yake gulma , kace dashi: yaji tsoron Allah.
24-ka dawwamar da kanka wurin karanta suratul MULK domin tana tseratarwa.
25- wanda aka hana( yayi hasara) shine wanda aka hanawa sallar dake cike da tsoron Allah , da idon dake zubar da hawaye.
26- kar ka cutar da bayin Allah nagari wadanda suka shagaltu da bautar Allah.
27- ka sanya soyayyar ka duka zuwa ga Allah da manzonsa.
28- ka yafewa wanda yayi gulmarka, domin ya baka kyautar kyakyawan aikinsa ne.
29- Sallah da ambaton Allah da karatun alqur'ani alqawurane masu nauyi akan qirjinka.
30- duk wanda ya tuna da zafin wuta zai iya hakuri akan sabon Allah .
31- indai ana dare gari yana wayewa, to watarana sai labari tsanani zai zama sauqi.
32- ka nisanci ANCE-KACE ( jita-jita) domin kai game da ayyuka kamar dutsene.
33- kayi sallah da tsoron Allah , domin duk abun da zakayi bayan sallar bai kai sallah ba.
34- ka sanya alqur'ani daf dakai , domin karanta aya daya acikinsa yafimaka duniya da abun dake cikinta.
35- rayuwa akwai dadi, mafi dadin rayuwa shine kaganka da iimaninka.


Ku biyo mu a shafin mu na Facebook @isyakuweb https://web.facebook.com/isyakuweb Kana sha'awar ka sami labaranmu ta Whatsapp ? ka rubuto YES a Whatsapp zuwa 08062543120 zamu aiko maka da Labaran mu kai tsaye kyauta a koda yaushe muka wallafa Labari. Kana da sha'awar taimaka mana da Labarai, ko sharhi ? ka kira mu a 08062543120. Shiga shafinmu kai tsaye domin samun cikakkun Labarai.Ka shiga www.isyaku.com a browser ko opera ko firefox ko safari na wayarka zaka sami cikakken shafinmu da ke dauke da ababe masu kayatarwa.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN